in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen dake yankin kahon Afirka sun yi alkawarin ba da goyon baya kan takaita kaurar jama'a
2019-05-09 10:05:38 cri

A jiya ne kasashen dake yankin kahon Afirka, suka yi alkawarin ba da goyon baya don takaita kaurar jama'a, ta yadda za a samu zaman lafiya da kwanciyar hankali da ma ci gaban da ake bukata.

Darektan sashen lafiya da ci gaban walwalar jama'a a hukumar raya kasashen gabashin Afirka (IGAD), shi ne ya bayyana hakan a birnin Nairobin kasar Kenya, yayin da yake jawabi a bikin bude taron kasa da kasa kan yadda ake tilastawa jama'a barin matsugunansu. Yana mai cewa, daidaita wannan matsala, za ta yi kyakkyawan tasiri ga tattalin arziki da yanayin zaman takewar jama'a.

A don haka, ya bukaci da a bullo da managartan manufofi da dokoki, domin kare da kuma baiwa al'ummomin dake fadawa cikin wannan matsala 'yanci tare kuma da kara gina al'ummomin da wannan matsala ta shafa.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China