in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta damu da rahotannin kai hare-hare ta sama kan cibiyoyin fararen hula a Syria
2019-05-07 14:19:22 cri

Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya damu da rahotannin kai hare-hare ta sama kan cibiyoyin fararen hula a Syria.

Guterres ya bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa ya rabawa manema labarai. A ranar 5 ga watan Mayu ne, aka ba da rahoton kai hare-hare ta sama kan wasu cibiyoyin kiwon lafiya 3, adadin da ya karu zuwa cibiyoyin kiwon lafiya a kalla 7 ke nan da aka kai irin wadannan hare-hare tun a ranar 28 ga watan Afrilu.

Bugu da kari, an ba da rahotan kai irin wadannan hare-hare kan makarantu 9 a ranar 30 ga watan Afrilu, an kuma rufe wasu karin makarantu a galibin yankunan kasar, har sai baba ta gani.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China