Yanzu haka dai wakilin musamman na babban magatakardar MDD a yammacin Afirka da yankin Sahel Mohamed Ibn Chambas, ya fara tattaunawa da sauran sassa masu ruwa da tsaki daga kungiyar bunkasa tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka, da kuma masu fada a ji na Benin, a wani mataki na karfafa gwiwar daukar matakan warware takaddamar da ta kunno kai a kasar cikin lumana. (Saminu Hassan)