in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalissar sojoji dake rikon kwarya a Sudan ta sha alwashin ci gaba da tattaunawa da kaucewa yamutsi
2019-05-01 15:45:18 cri
Majalissar sojoji dake rikon kwarya a kasar Sudan ko TMC a takaice, ta sha alwashin ci gaba da tattaunawa da daukacin sassan masu ruwa da tsaki game da yanayin siyasar kasar, tana mai cewa za ta dauki dukkanin matakan da suka wajaba, na kaucewa yamutsi da karya doka.

Da yake karin haske game da batun zaman dirshan da masu zanga zanga suke ci gaba da gudanarwa a birnin Khartoum, fadar mulkin kasar, mataimakin shugaban majalissar ta sojoji Mohamed Hamdan Daqlu, ya ce sojoji ba za su tarwatsa masu zanga zangar ba.

A ranar Litinin ne dai TMC da jagororin kungiyoyin 'yan adawa a kasar, suka kammala zaman tattaunawa na uku ba tare da cimma wata yarjejeniya, ta yadda za a kafa gwamnatin farar hula ba.

Bayan tattaunawar ranar Litinin, gungun hadakar 'yan adawar kasar sun yi kira ga 'yan kasar, da su ci gaba da zaman dirshan, tare da gudanar da zanga zangar dare a birnin Khartoum. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China