Osman Saleh, Ministan harkokin wajen kasar Eritrea zai kawo wa kasar Sin ziyara daga ranar 5 zuwa 10 ga watan Mayun bana bisa gayyatar da takwaransa na kasar Sin Wang Yi ya yi masa, kamar yadda Geng Shuang, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, ya sanar yau Talata a nan Beijing. (Tasallah Yuan)