Wata sanarwa da ofishin shugaban kasar ya fitar, ta bayyana cewa, dokar hana rufe fuskar za ta fara aiki ne tun daga yau Litinin, karkashin sabbin matakan da suka kai ga sanya dokar ta baci a kasar, domin mayar da martani ga hare-haren bama-baman da suka kai ga kisan sama da mutane 250 tare da jikkata sama da mutane 500. (Ibrahim Yaya)