in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jagoran Hamas ya yi kira ga al'ummar Palasdinu su hada kansu don tinkarar yarjejeniyar Amurka
2019-04-28 16:36:56 cri
Jagoran kungiyar Hamas, Ismail Haniya ya bayyana a jiya Asabar a birnin Gaza cewa, ya kamata sassa daban daban na Palasdinu su hada kansu kuma su cimma daidaito a tsakaninsu, don tinkarar yarjejeniyar karni da Amurka za ta gabatar.

A yayin da yake ganawa da shugabannin wasu jam'iyyun Palasdinu a zirin Gaza, Ismail Haniya ya ce, a shirye yake ya gana da jam'iyyu daban daban, musamman ma kungiyar Fatah, don farfado da hadin kai a tsakaninsu.

Tun bayan da Donald Trump ya rike karagar mulkin Amurka, ya fara tunanin yarjejeniyar karni, don wanzar da zaman lafiya a tsakanin Palasdinu da Isra'ila. Sai dai a kwanakin baya, wakilinsa na musamman kan shawarwari, Jason Greenblatt ya fayyace cewa, yarjejeniyar ba za ta kunshi abin da ya shafi kafa kasashe biyu bisa shatin iyakar shekarar 1967 ba. Sau da dama, Palasdinu ta ce ba za ta amince da yarjejeniyar ba, sabo da ba ta shafi batun Kudus da matsalar 'yan gudun hijirarta da kuma matsugunan Yahudawa ba. (Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China