Shugaban kasar Cyril Ramaphosa da ya halarci bikin ya bayyana a jawabin da ya gabatar cewa, shekaru 25 da suka wuce, al'ummar kasar Afirka ta kudu suka kafa wata sabuwar kasar da ke da zaman daidaito da hadin kan al'umma, inda kuma ba a nuna bambanci ga kabilu da jinsi daban daban, yana mai cewa, rana ce ta walwala ga dukkan al'ummar kasar. Shugaban ya kuma yi alkawarin tabbatar da 'yancin al'ummar kasarsa na jin dadin bunkasar tattalin arziki da zaman rayuwarsu. (Lubabatu)