in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin 'yan sandan kasashen gabashi da tsakiyar Afirka na taron yaki da safarar bil-Adama a Tanzaniya
2019-04-26 10:19:30 cri
Shugabannin 'yan sanda daga kasashen gabashi da tsakiyar Afirka, na wani taro a kasar Tanzaniya, don lalubo matakan yaki da manyan laifuffuka da ake aikatawa a kan iyakokin kasashen, ciki har da fatauncin bil-Adama da ma laifukan da ake aikatawa ta yanar gizo.

Taron dake gudana a birnin Dar-es Salaam, cibiyar kasuwancin kasar, ya hallara manyan sifetocin 'yan sandan kasashen Tanzaniya mai masaukin baki, da Kenya, da Rwanda da kuma Mozambique.

A jawabinsa na bude taron, babban sifeton 'yan sandan kasar Tanzaniya Simon Sirro, ya ce taron ya samar musu da wani dandali na bullo da matakan yaki da daukar kwararan tsari na doka kan laifukan da ake aikatawa a yankin da ma kasashensu.

Ya ce, sun dade suna aiki tare a fannoni daban-daban, suna kuma kokarin fito da wasu dabaru da za su taimaka wajen gano tare da magance manyan laifukkan da ake aikata a kan iyakokin kasashen.

A cewar Sirro, hadin gwiwar da suke yi, za ta taimaka wajen bankado maboyar wadanda ake zargi.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China