in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tunisia na karban bakuncin taro kan daidaiton jinsi
2019-04-25 14:20:58 cri
Sama da jami'ai 400 daga Tunisia da sauran kasashen duniya ne suka hadu a jiya Laraba, domin halartar taro kan daidaiton jinsi.

Gwamnatin Tunisia da shirin raya kasashe na MDD da hukumar kula da mata ta MDD ne suka shirya taron, wanda zai gudana har zuwa gobe Juma'a.

A jawabinta na bude taron, Ministar kula da harkokin mata da iyali da yara ta Tunisia, Neziha Labidi, ta ce taron da ake a Tunisia kan daidaiton jinsu, ya nuna yadda kasashen duniya ke sane da kokarin kasar na inganta daidaiton jinsi da hakkokin mata.

Ta kara da cewa, taron dama ce ta bayyana kyakkyawan matsayin Tunisia, inda maza da mata ke aiki tare domin ci gaban kasar, kana kuma take tabbatar da daidaton damarmaki tsakaninsu.

Ta ce dole ne a dakatar da take hakkin mata, ta na mai cewa dole ne dukkan matan kasar, su hada kansu karfafa bada gudunmuwa wajen yanke shawarwari da kuma kasancewarsu kan mukamai. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China