in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Habasha za ta zurfafa hadin gwiwa da Kasar Sin
2019-04-25 10:05:08 cri
Gwamnatin Habasha ta jaddada kudurinta na karfafa hulda da kasar Sin karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da kuma dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika.

Wata sanarwa da ofishin Firaministan kasar Abiy Ahmed ya fitar ce ta bayyana haka a jiya.

Sanarwar ta ruwaito Abiy Ahmed na cewa, layin dogon da ya hada Addis Ababa da Djibouti sakamako ne na farko-farko da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya da Habasha ke ciki, ta haifar.

Ofishin ya bayyana ziyarar Firaminista Abiy Ahmed a kasar Sin, wanda wani bangaren ne na shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, a matsayin mai muhimmanci, yana mai cewa, tuni ziyarar ta haifar da kyawawan sakamako ga kasar dake gabashin Afrika. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China