in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi suka da kakkausar murya kan hare-haren da aka kai a Sri Lanka
2019-04-23 19:21:35 cri

Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya bayyana a yayin taron ganawa da manema labaran da aka saba yi a nan birnin Beijing a yau din nan cewa, kasar Sin ta yi suka da kakkausar murya, game da jerin hare-haren da aka kaddamar a kasar Sri Lanka, haka kuma tana son yin kokari tare da sauran kasashen duniya, domin kara karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu a bangaren yaki da ta'addanci, tare kuma da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a shiyya shiyya, da kuma duk fadin duniya.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, bayan hare-hare sau takwas da aka kai a kasar ta Sri Lanka, hukumar 'yan sandan kasar ta gano, ta kuma rushe na'urar boma-bomai ta tara da aka girke cikin nasara.

Geng Shuang ya kara da cewa, gwamnatin kasar Sin za ta ci gaba da dora muhimmanci kan wannan lamarin. (Jamila)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China