in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar sojin wucin gadi ta Sudan ta kori wasu jakadu 6
2019-04-23 09:32:41 cri
A jiya ne majalisar sojojin wucin gadi dake Sudan, ta yanke shawarar sake yiwa jakadunta dake aiki a kasashen wajen garambawul tare da sallamar wasu guda 6.

Majalisar ta bayyana cikin wata sanarwa cewa, ta ba da wasu shawarwari masu muhimmanci da kuma dokoki bisa kundin tsarin mulki dangane da yiwa hukumomin kasar gyaran fuska ciki har da dakatar da wasu jakadu daga aiki.

Bugu da kari, majalisar ta yanke shawara a yayin ganawar da ta yi jiya Litinin, don sake nazartar kudaden ketare da aka kashe da kudaden harajin fitar da kayayyaki dake babban bankin kasar

Aikin majalisar wadda karkashin jagorancin Abdel-Fattah Al-Burhan dai, shi ne tafiyar da harkokin kasar, bayan kifar da gwamnatin shugaba Omar a-Bashir. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China