in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU za ta kaddamar da wani shiri na raya matasan Afirka
2019-04-23 09:25:33 cri

Shugaban hukumar gudanarwar kungiyar tarayyar Afirka (AU) Moussa Faki Mahamat, ya bayyana cewa, kungiyar tana shirin kaddamar da wani sabon shiri , mai suna, "miliyan 1 nan da shekarar 2021" da nufin samar da damammaki da za su kai ga inganta rayuwar matasa a Afirka, ta yadda za a kai ga cimma nasarar ajandar raya nahiyar nan da shekarar 2063.

Moussa Faki ya bayyana hakan ne yayin da yake kaddamar da sabon shirin nahiyar, wanda ke bukatar zage damtse tsakanin kasashen mambobin kungiyar,da hukumomin kungiyar da ma ragowar masu ruwa da tsaki,idan har ana son shirin ya kai ga gacci.

Kungiyar ta ce, manufar sabon shirin, ita ce, samar da damammaki ga matasa miliyan guda dake sassan nahiyar daban-daban, a muhimman fannoni da suka hada da aikin yi,da sana'o'i, Ilimi da shiga a dama da su a wadannan fannoni hudu(4E's), matakan da za su hanzarta bunkasar rayuwa da tattalin arziki a nahiyar.

A gobe ne dai ake sa ran kaddamar da sabon shirin a hedkwatar kungiyar ta AU dake birnin Addis Ababa na kasar Habasha a hukumance.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China