in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Afirka ta kudu zai ba da muhimmanci ga batun zaman lafiyar shiyyar yayin taron AU na Masar
2019-04-23 09:06:02 cri
Shugaban kasar Afirka ta kudu Cyril Ramaphosa, zai ba da muhimmanci ga batun zaman lafiya da kwanciyar hankalin shiyya, yayin taron kolin kasashe uku na kungiyar tarayyar Afirka (AU) game da batun rikicin kasashen Sudan da Libya da zai gudana a kasar Masar.

Mai magana da yawun fadar shugaban kasar Afirka ta kudu Khusela Diko wanda ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai jiya Litinin, ya ce, shugaba Ramaphosa zai halarci taron gaggawan da za a kira, domin ba da gudummawa ga manufar da AUn ke fatan cimmawa na kawar da karar bindigogi a nahiyar nan da shekarar 2020.

Sanarwar ta ce, shugaba Ramaphosa zai halarci taron kolin Masar, inda zai mayar da hankali kan yanayin siyasa sa tsaro da ake fama da shi a kasashen Libya da Sudan.

Shugaba Abdel-Fattah al-Sisi na kasar Masar, ya kira taron ne a matsayinsa na shugaban karba-karba na kungiyar AU. Shi dai taron AU na Masar din, ya kunshi kasashen Masar kasancewar mai rike da shugabancin karba-karba, da Afirka ta kudu, mai jiran gadon shugabancin karba-karba na kungiyar, sai kuma Rwanda wanda wa'adinta shugabancinta ya kare.

Taron kolin zai kuma samu halartar shugaban hukumar gudanarwar kungiyar Moussa Faki Mahamat, wanda ake sa ran zai gabatar da rahoto game da matakan da kungiyar ta dauka na daidaita rikicin kasashen Sudan da Libya. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China