Rahotanni farko, sun bayyana cewa, adadin wadanda suka mutu sun kai 228, kana 450 kuma suka jikkata a hare-hare guda takwas din da aka kai ranar Lahadi a majami'u uku da otel-otel guda hudu dake sassan kasar.
Wata sanarwa da hukumar raya harkokin yawon shatakawa ta kasar ta fitar jiya Lahadi, ta bayyana cewa, baki 'yan kasashen waje 32 na daga cikin wadanda suka mutu, sanadiyar wadannan hare-hare.(Ibrahim)