in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kama mutane 13 dangane da fashewar da ta auku a Sri Lanka
2019-04-22 10:34:17 cri

Rundunar 'yan sandan kasar Sri Lanka ta bayyana cewa, an kama mutane 13 dangane da jerin bama-baman da suka tashi a sassan tsibirin kasar, wadanda suka yi sanadin mutuwar mutane 228.

Rundunar 'yan sandan kasar, ta ruwaito rahotannin kafafen watsa labarai na cewa, an mika mutane 10 cikin 13 da aka kama a Colombo, babban birnin kasar ga sashen binciken manyan laifuffuka.

Firaministan kasar Ranil Wickremesinghe ya shaidawa manema labarai cewa, mutanen da aka kama 'yan kasar Sri Lanka ne, ana kuma gudanar da bincike don kara gano wadanda ke da hannu a tashin abubuwan fashewar.

Ya ce, kimanin mutane 228 ne aka tabbatar sun mutu kana wasu 450 kuma sun jikkata, sanadiyar abubuwan fashewa takwas din da suka tashi a jiya Lahadi. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China