in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na maraba da gudanar da tattaunawa a tsakanin majalisar soji ta wucin gadin kasar Sudan da bangarori daban daban na kasar
2019-04-17 20:59:00 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya ce, kasa sa tana goyon bayan majalisar soji ta wucin gadin kasar Sudan da ta soma gudanar da tattaunawa tare da bangarori daban daban na kasar don sauraron ra'ayoyinsu.

Lu ya bayyana haka ne a yayin taron manama labaru da aka shirya a yau Laraba.

Kwanan baya ne, aka kafa majalisar soji ta wucin gadin kasar Sudan, tare da mika mulki cikin shekaru 2, inda suka yi alkawarin cewa, za a kafa gwamnatin fararen hula da za ta samu amincewar bangarori daban daban, wadda za ta mika mulki bayan kammala wa'adinta na mika mulki. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China