in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin: kasashen Afirka ba za su amince da matakan Japan na tabo batun bashin da ake bin su ba
2019-04-17 20:53:39 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya ce, kasar Sin tana maraba, kana kofarta a bude take ga abokan huldar kasa da kasa na karfafa hadin gwiwa da kasashen Afirka. Amma idan bangaren Japan, ya mai da batun bashin da ake bin kasashen Afirka bisa ra'ayi na siyasa ko wani kokari na bata sunan kasar Sin, to, kasashen Afirka ba za su yarda da haka ba.

Lu ya bayyana haka ne a yayin taron manema labaru da aka shirya a yau Laraba.

Bayanai na cewa, gwamnatin Japan ta shirya aika kwararru a fannin kudi zuwa kasashen Afirka da suka karbi bashi daga kasar Sin, don taimaka musu warware matsalar kudin da suke fuskanta, kuma tana shirin gabatar da hakan a yayin taron kasa da kasa kan batun ci gaban Afirka da za a yi a birnin Tokyo a watan Agustan bana. Game da haka, Lu ya ce, yanzu kasashen Afirka na kokarin gaggauta bunkasa tattalin arziki da al'ummansu, kuma matsalar rashin kudi matsala ce da suke fuskanta. A matsayinta na abokiyar kasasen Afirka, kasar Sin na fatan karfafa hadin kai da kasashen Afirka a fannonin zuba jari da harkokin kudi, da kokarin taimakawa kasashen Afirka kan yadda za su kyautata muhimman kayayyakin more rayuwa da yanayin ci gaban tattalin arziki da na al'umma, don kara karfinsu da neman ci gaba. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China