in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Sin ya gana da takwaransa na Burkina Faso
2019-04-17 20:21:14 cri
Yau Laraba, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da takwaransa na kasar Burkina Faso Alpha Barry a nan birnin Beijing.

A yayin ganawar, Wang ya bayyana cewa, shekara guda bayan farfado da huldar diplomasiyya a tsakanin Sin da Burkina Faso, kasashen biyu sun samu muhimmiyar nasara a fannin hadin gwiwa da juna. A cewar Wang, kasarsa tana goyon bayan matakan da Burkina Faso take dauka wajen neman ci gaba dake dacewa da halin da take ciki, da kokarin da gwamnatin kasar ke yi wajen kiyaye tsaro, bunkasa tattalin arziki da kuma kyautata zaman rayuwar jama'a.

Kasar Sin tana kuma fatan karfafa hadin kai dare da Burkina Faso bisa tsarin shawarar "Ziri daya da hanya daya", da tsarin dandalin tattaunawar hadin kai a tsakanin Sin da kasashen Afrika.

A nasa bangaren Barry ya bayyana cewa, kudurin da kasarsa ta yanke na farfado da huldar diplomasiyya tare da kasar Sin ya yi daidai. Kasar Burkina Faso na son karfafa hadin kai tare da Sin bisa tsarin shawarar "Ziri daya da hanya daya". (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China