in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Syria ya bukaci a karfafa huldar dake tsakanin kasarsa da kasar Iraki
2019-04-15 10:33:44 cri
Shugaban kasar Syria Bashar al Assad ya bayyana a jiya Lahadi cewa, karfafa huldar dake tsakanin Syria da Iraki zai taimakawa tabbatar da moriyar jama'ar kasashen 2, gami da kokarin dakile ta'addanci.

Rahoton kamfanin dillancin labarai na kasar Syria ya ruwaito cewa, shugaba Bashar, ya gana da al-Falih Faryadi, mai ba da shawara kan ayyukan tsaron kasar Iraki, wanda ya kai ziyara kasar Syria, a jiya. Inda shugaban kasar Syria ya ce, yanayin da ake fuskanta a yankin da kasashen 2 suke ciki, gami da daukacin duniya, na bukatar kasashen Syria da Iraki su yi kokarin kare mulkin kai da 'yancin tsara manufa bisa ra'ayin kansu, a lokacin da suke fuskantar abokan gaba, wadanda ke son ganin barakar kasashen, gami da tashin hankali a cikinsu.

Ban da haka, bangarorin 2 sun tattauna hanyar da za a bi wajen kyautata huldar dake tsakanin kasashen 2, tare da jaddada wajibcin raya huldar daga dukkan fannoni.

A nashi bangare, al-Falih Faryadi ya ce, yadda kasar Syria ta samu dakile ta'addanci wata nasara ce a bangaren kasar Iraki, yayin da duk wani ci gaban da aka samu a matakin sojan da aka dauka a kasar Iraki, zai taimakawa samun kwanciyar hankali a Syria. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China