in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan za a kara taimakawa samun zaman lafiya a Gabas ta Tsakiya
2019-04-09 19:37:38 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Lu Kang, ya furta wajen wani taron manema labaru da ya gudana a yau a nan birnin Beijing na kasar Sin cewa, ana fata wasu kasashe, musamman ma wasu manya wadanda ke wajen yankin Gabas ta Tsakiya, za su kara kokarin taimakawa samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

A jiya shugaban kasar Amurka Donald Trump ya sanar da cewa, gwamnatinsa na shirin sanya rundunar sojojin kasar Iran ta IRG, cikin jerin sunayen kungiyoyin ta'addanci. Hakan zai zama karo na farko da kasar Amurka ta sanya rundunar sojojin wata kasa cikin jerin sunayen.

Dangane da batun, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya ce kamata ya yi a nuna biyayya ga ka'idojin huldar kasa da kasa, wadanda aka kafa su bisa tushen kundin tsarin mulkin MDD. Sa'an nan a magance daukar matakan nuna fin karfi, da bin ra'ayi na kashin dankali. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China