A yau ne shugaba Idriss Deby na kasar Chadi ya isa Khartoum, babban birnin kasar Sudan, don fara wata ziyarar aiki ta yini guda.
Shugaba Omar al-Bashir na Sudan da jami'an kasar da wakilan ofisoshin jakadancin kasashe daban-daban da dama dake Sudan ne suka tarbe shi a filin saukar jiragen saman kasar.
Ana sa ran shugabannin kasashen biyu, za su gana a fadar shugaban kasa, inda za su tattauna batutuwan shiyya da wadanda ke shafar su. Za kuma su tattauna kan bunkasa alaka tsakanin kasashen biyu a fannoni da dama.
Daga bisani shugabannin biyu, za su yiwa manema labarai bayanai game da sakamakon ziyarar.(Ibrahim)