in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi kira ga kasashen da suka mallaki makaman nukiliya su daina yakin cacar baka
2019-04-03 10:19:35 cri
Zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Ma Zhaoxu, ya yi kira ga kasashen da suka mallaki makaman nukiliya, su ajiye batun yakin cacar baka da ra'ayin samun riba kan asarar wani bangare, game da batun kawar da makaman nukiliya.

Ma Zhaoxu, ya bayyana haka ne yayin taron kwamitin sulhu na MDD dake goyon bayan yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya, gabanin taron bitar da za a yi a 2020.

Wakilin na Sin, ya ce ya kamata kasashen su daina amfani da dabarun kare kai da makaman nukiliya ta hanyar kai harin ba-zata, sannan su soke rawar da makaman ke takawa cikin dabarunsu na tsaron kasa.

Ya ce kasar Sin na kira musammam ga Rasha da Amurka, su ci gaba da warware sabanin dake tsakaninsu ta hanyar tuntubar juna da tattaunawa, tare da komawa ga kiyaye tanade-tanaden yarjejeniyar kawar da makaman nukiliya masu cin matsakaicin zango nan bada dadewa ba, sannan su lalubo hanyar tsawaita yarjejeniyar kawar da makaman nukiliya dake tsakaninsu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China