in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi gargadi game da take 'yancin kasa da sunan kai agaji
2019-04-02 10:45:15 cri
Zaunannen Wakilin kasar Sin a MDD, Ma Zhaoxu, ya yi gargadi game da yunkurin take cikakken 'yancin da ikon kasa kan yanukunta, ta hanyar amfani da agajin jin kai.

Yayin wata muhawara kan dokokin agajin jin kai na kasa da kasa da kwamitin sulhu na MDD ya yi, Ma Zhaoxu, ya yi kira ga kasashe su kiyaye manufofi da ka'idojin MDD tare da dokokin ayyukan jin kai.

Ya ce ya kamata dukkan hukumomin agaji su kiyaye dokokin bada agaji na kasa da kasa da sauran dokokin masu alaka, tare da kaurecwa amfani da kai agajin jin kai domin siyasa ko aikin soji ko kuma wasu manufofi.

Ya kuma bukaci a hada hannu wajen warware rikice-rikice cikin lumana, wanda zai kai ga shawo kan matsalolin kare fararen hula tun daga tushe. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China