Da take jawabi jiya, yayin taron kungiyar kawancen Larabawa karo na 30 da aka yi a birnin Tunis na Tunisia, wakiliyar EU kan harkokin diflomasiyya da tsaro, Federica Mogherini ta ce matakin na Amurka, ya kaucewa kudurorin Kwamitin sulhu na MDD wadanda ke daukar Tuddan Golan a matsayin yankin Syria da Isra'ila ta mamaye. (Fa'iza Mustapha)