in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan majalisar dokokin Birtaniya sun kada kuri'ar sauya ranar yarjejeniyar ficewar kasar daga tarayyar Turai
2019-03-28 10:21:36 cri

A ranar laraba 'yan majalisar dokokin Birtaniya suka amince da sauya ranar yarjejeniyar ficewar kasar daga tarayyar Turai zuwa 12 ga watan Afrilu ko kuma 22 ga watan Mayu a yayin da ya rage sa'oi 11 kan bukatar da firaiministar Birtaniyan Theresa May ta mika don neman goyon bayan majalisar dokokin kasar kan yarjejeniyar ficewar kasar.

'Yan majalisar 441 sun yi galaba kan takwarorin 105 a zauren majalisar wajen gabatar da sabuwar ranar yarjejeniyar ficewar kasar, kana sun yi watsi da ainihin ranar da aka tsara Birtaniyan zata fice daga tarayyar Turai wato 29 ga watan Maris.

Tun da farko a ranar Laraba, May ta shedawa 'yan majalisar dokoki kasar cewa zata sauka daga matsayinta na firaiministar idan 'yan majalisar dokokin kasar suka goyi bayan bukatar data gabatar musu, wanda suka yi fatali da ita har sau biyu tun daga watan Janairu.

A bukatar data gabatawar 'yan majalisar dokokin bangaren Tory na neman amincewarsu ga bukatar data mikawa majalisar dokokin game da yarjejeniayar ficewar kasar, firaiministar tace, a shirye take ta sauka daga kan kujerarta tun ma gabanin lokacin da ta shirya yin murabus din. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China