Kwamitin sulhun MDD, ya taya Guinea-Bissau murna kan yadda aka gudanar da zaben majalisar dokokin kasar na ranar 10 ga watan Mayun wannan shekara cikin lumana.
Cikin wata sanarwa da ya fitar, kwamitin sulhun ya taya gwamnati da al'ummar kasar da jam'iyyun siyasu, da ma kungiyoyin fararen hula, murnar yadda aka gudanar da zabukan ba tare da wani tashin hankali ba.(Ibrahim)