in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Guterres: Mahaukaciyar guguwar Idai ta halaka mutane a kalla 700
2019-03-27 10:01:58 cri

Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya bayyana cewa, mahaukaciyar guguwar Idai, da ta aukawa kasashen Mozambique da Zimbabwe da Malawi, ta halaka mutane a kalla 700.

Guterres wanda ya bayyana hakan a jiya Talata, ya kuma yi kira ga kasashen duniya, da su agazawa kasashen da iftila'in ya shafa da gudummawar dala miliyan 281.7.

Jami'in na MDD ya ce, yawan wadanda suka mutu a kasashen uku, ya kai a kalla 700, baya wasu daruruwa da suka bace. An kuma yi kiyasin mutane miliyan 3 da bala'in ya shafa, kusan kaso biyu bisa uku na wannan adadi ya shafi kasar Mozambique ne.

Mahaukaciyar guguwar Idai mai tafe da iska da ruwan sama, na daya daga cikin bala'u da nahiyar ta fuskanta a tarihi. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China