in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi ya bukaci a dauki dukkan matakan da suka dace don ceto wadanda hadarin fashewar da aka auku a rukunin masana'antu dake lardin Jiangsu
2019-03-22 19:31:08 cri
Shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya bukaci da a dauki dukkan matakan da suka wajaba na ganin an gano tare da ceto wadanda ke da sauran numfashi, bayan hadarin fashewar da ta faru a rukunin masana'antu a lardin Jiangsu dake gabashin kasar Sin, inda mutane 47 suka mutu kana wasu mutane 90 kuma suka jikkata.

Xi, wanda har ila shi ne babban sakataren kwamitin koli na JKS, kana kwamandan askarawar kasar, ya ba da wannan umarni ne yayin da yake rangadin aiki a kasashen wajen.

Shugaba Xi ya ce, wajibi ne a dauki dukkan matakai na ganin an gano wadanda suka makale, kana a yiwa wadanda suka jikkata magani a kan lokaci, haka kuma wajibi ne a gudanar da aikin ceto yadda ya kamata don ceton rayukan jama'a.

A halin da ake ciki kuma, ya kamata a inganta yanayin sanya-ido da matakan gargadi domin kare gurbatar muhalli da aukuwar manyan bala'u.

Hukumomin yankin sun bayyana cewa, fashewar ta faru ne da misalin karfe 2 da mituna 48 na ranar Alhamis agogon wurin , bayan da wata gobara ta tashi a dakin adana sinadarai dake rukunin masana'antar, lamarin da ya haddasa jikkata da hasarar rayuka. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China