in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'an MDD sun bukaci a gaggauta kawo karshen wariyar launin fata
2019-03-22 16:40:36 cri
Jami'an MDD biyu, masu rajin kare hakkin dan Adam sun bukaci kasashen duniya su gaggauta daukar matakin tabbatar da daidaito tsakanin masu launin fata daban daban tare da dakatar da amfani da asali wajen nuna wariya.

Jami'an biyu da suka hada da babban mai bayar da rahoto kan batun wariyar launin fata na MDD Tendayi Achiume, da shugaban ayarin kwararru dake aiki kan al'ummar Afrika Micheal Balcerzak ne suka yi kiran a ranar yaki da wariyar launin fata ta duniya, wadda ake yi a duk ranar 21 ga watan Maris din kowacce shekara.

Kwararrun biyu sun kuma soki hare-haren da aka kai wata masallaci a kasar New Zealand, wadanda suka yi sanadin mutuwar mutane 50 da raunana wasu da dama

Sun jaddada cewa, dole ne kasashe su gaggauta daukar mataki don rage tsana da wariya domin kare mutane masu rauni da kuma tabbatar da daidaito tsakanin mabanbanta fata. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China