in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya jajantawa takwarorinsa na Mozambique, Zimbabwe da Malawi
2019-03-21 19:25:26 cri
Jiya Laraba 20 ga wata, shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya aika da sakonni ga takwarorinsa na kasashen Mozambique, Zimbabwe da Malawi, inda ya janjanta musu kan barnar da mahaukaciyar guguwar nan ta Idai ta haddasa a kasashensu.

A cikin sakonsa, shugaban kasar Sin ya ce, mahaukaciyar guguwa ta Idai ta yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama tare da raunata wasu da haddasa asarar dukiyoyi a kasashen Mozambique, Zimbabwe da Malawi. A madadin gwamnatin kasar Sin da jama'ar kasar, da kuma shi kansa, shugaba Xi ya nuna damuwarsa kan wannan bala'i, kana ya jajantawa iyalan wadanda suka mutu da wadanda suka bace, da wadanda suka ji rauni, da ma wadanda bala'in ya rutsa da su. Yanzu jama'ar kasashen 3 suna fama da radadin wannan bala'in. Kasar Sin ta fahimci kuncin da suke ciki sosai. Ya yi imanin cewa, a karkashin shugabancin gwamnatocin kasashen 3, jama'arsu za su jure kuncin bala'in, za su kuma sake gina gidajensu cikin sauri. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China