Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya bar birnin Beijing a yau Alhamis, domin ziyarar aiki a kasashen Italiya da Monaco da Faransa, daga yau 21 zuwa 26 ga wata. Wannan ita ce tafiya ta farko da shugaban ya yi zuwa ketare tun farkon shekarar bana. (Fa'iza Mustapha)