A cikin sakonsa, Wang Qishan ya bayyana cewa, a cikin 'yan shekarun da suka gabata, dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a tsakanin kasashen Sin da Najeriya na samun ci gaba a dukkan fannoni, kuma an cimma manyan nasarori. A cewar Wang Qishan, yana fatan hada kai tare da Yemi Osinbajo, don ciyar da kyakkyawar dangantakar hadin kai dake tsakanin kasashen biyu gaba, ta yadda za a kara samar da alheri ga jama'ar kasashen biyu. (Bilkisu)