in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin kasahen duniya sun bukaci a dauki matakan kiyaye muhalli
2019-03-15 10:26:16 cri
Shugabannin kasashen duniya da hukumomin gwamnati wadanda ke halartar babban taron hukumar kare muhalli ta MDD karo na hudu (UNEA) a Nairobi, sun sake yin kiran a aiwatar da matakai mafiya dacewa domin yaki da sauyin yanayi, da gurbata muhalli, da kuma lalata muhallin halittu.

Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta, da takwarorinsa na kasashen Faransa, Sri Lanka, Madagascar, da jamhuriyar demokaradiyyar Kongo (DRC), sun bi sahun wakilai mahalarta taron wajen amincewa da daukar kwararan matakai cikin gaggawa wadanda zasu tabbatar da kyautatuwar muhalli da samar da dawwamamman cigaba a nan gaba.

"Dole ne mu gaggauta sauya yadda ake gurbata muhalli wanda lamarin ke kara yin tsanani sakamakon halayyar da ake nunawa ta dakile cigaba mai dorewa," inji Kenyatta, ya kara da cewa, lalata muhalli shine musabbabin dake haifar da karuwar talauci da rashin wadataccen abinci.

Kenyatta yace, aiwatar da shirye shirye da suka kunshi zuba jari a fannin samar da fasahar makamashi mai tsabta da yin kirkire kirkire sune manyan jigo wajen kaucewa gurbata muhalli da kyautata muhallin halittu kamar kyautata hukumomin kula da dazuka da ingancin ruwa.

Macron a jawabinsa yace, gaggauta daukar matakai na gamayyar kasa da kasa muhimmin mataki wajen dakile baraznar da muhalli ke fuskan wanda ke da alaka da hallayar bil adama.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China