in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNEP ta bukaci kasashen Afrika su dauki matakan kare yankuna masu dausayi a nahiyar
2019-03-14 10:44:18 cri

Shirin kare muhalli na MDD (UNEP) ya bukaci kasashen Afrika da su dauki kwararan matakai na kare yankuna masu dausayi a nahiyar

Joakim Harlin, shugaban sashen kula da tsabtar ruwa na muhallin hallitu na hukumar ta UNEP, ya fadawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua a Nairobi cewa, wurare masu dausayi muhimman arziki ne musamman bisa ga irin gudunmowar da suke bayarwa wajen samar da muhalli mai tsabta. Ya kamata gwamnatocin kasashen Afrika su sanya dokoki da za su magance lalata yankuna masu dausayi, inji Harlin, ya bayyana hakan ne a gefen taron kare muhalli na MDD (UNEA) karo na hudu a birnin Nairobi.

Ya kara da cewa, ya kamata a samar da dokokin da za su taimaka wajen bada kariya daga illata yankuna masu dausayi.

A ceware jami'in hukumar ta UNEP, yadda mazauna yankunan karkara ke lalata yankuna masu dausayi da kuma wasu ayyukan masana'antu suna daga cikin manyan barazanar dorewar yankuna masu dausayi a nahiyar Afrika. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China