in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban jami'in MDD ya yi Allah wadai da harin da aka kai cibiyar yaki da cutar Ebola a DRC
2019-03-12 10:23:00 cri

Sakataren janar na MDD Antonio Guterres ya yi Allah wadai da babbar murya game da harin da aka kaddamar kan cibiyar yaki da cutar Ebola a jamhuriyar demokaradiyyar Kongo (DRC), in ji Stephane Dujarric kakakin babban sakataren MDD.

Wasu rahotannin da aka wallafa sun nuna cewa an kashe wani jami'in dan sanda guda, kana an harbi wani ma'aikacin lafiya, sai dai ana sa ran zai iya farfadowa, harin dai an kaddamar da shi ne a ranar Asabar a gabashin birnin Butembo dake DRC.

Kakakin MDD ya fadawa manema labarai cewa shugaban hukumar lafiya ta duniya (WHO), Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ziyarci cibiyar bayan harin da aka kaddamar a ranar Asabar. An kuma kaddamar da wani harin a makon da ya gabata, in ji hukumar ta WHO.

Ziyarar na zuwa ne yayin da babban jami'in lafiya na MDDr ke kammala ziyararsa ta aiki na kwanaki uku a kasar, inda ya gana da wasu jami'an gwamnatin kasar, da kungiyoyin bada agaji masu zaman kansu na ciki da wajen kasar.

Ya bayyana fargaba game da hasarar rai da kuma jikkatar mutane da aka samu a sandiyyar hare-haren. Ya ce ba su da wani zabi da ya rage illa ci gaba da ceto rayukan jama'a a wannan waje, inda ya bayyana wajen a matsayin daya daga cikin wurare mafiya hadari a duniya. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China