in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya mika sakon ta'aziyya ga shugabar Habasha da na Kenya domin hadarin jirgin sama na Habasha
2019-03-11 20:37:18 cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika sako ga shugabar kasar Habasha Sahle-Work Zewde da shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta a yau Litinin mai kushe da ta'aziyya ta mutanen da suka mutu a sakamakon hadarin jirgin saman kamfanin zirga-zirgar jiragen saman kasar Habasha.

A cikin sakon, shugaba Xi Jinping ya bayyana cewa, ya samu labarin abkuwar hadarin jirgin sama a kasar Habasha, wanda ya haddasa mutuwar mutane da dama ciki har da mutanen kasashen Habasha da Kenya da Sin, don hakan a madadin gwamnatin kasar Sin da jama'arta da kuma shi kansa, Xi ya gabatar da ta'aziyyar mutanen da suka mutu a sakamakon hadarin, da jajantawa iyalansu. Ya kuma yi imanin cewa, gwamnatin kasar Habasha za ta gudanar da ayyuka bayan abkuwar hadarin yadda ya kamata, kana Sin za ta samar da gudummawa bisa bukatunta. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China