in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na MDD ya yi jimamin faduwar jirgin kasar Habasha
2019-03-11 11:29:23 cri
Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya yi jimamin faduwar jirgin sama, a kusa da Addis Ababa babban birnin kasar Habasha.

Wata sanarwa da kakakinsa Stephane Dujarric ya fitar, ta ce Antonio Guterres ya yi jimamin aukuwar mummunan lamarin da ya haifar da asarar rayuka.

Sakatare Janar din Ya kuma jajanta tare da mika ta'aziyyarsa ga iyalai da makusantan wadanda lamarin ya rutsa da su, ciki har da na jami'an MDD da kuma gwamnati da al'ummar Habasha.

Sanarwar ta kara da cewa, MDD na tuntubar hukumomin Habasha, kuma suna aiki tare domin samar da bayanan jami'an majalisar da hatsarin jirgin ya rutsa da su.

Da safiyar jiya Lahadi ne dukkan mutane 157 dake cikin jirgin saman Ethiopian suka mutu sanadiyyar hatsarin da jirgin ya yi.

Jirgin samfurin Boeing 737-800MAX, da ya nufi Nairobin Kenya, ya tashi ne da misalin karfe 8:38 na safe agogon Habasha, daga birnin Addis Ababa, da misalin karfe 08:44 ne kuma aka kasa tuntubarsa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China