in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashe masu tasowa sun yi kira ga majalisar kare hakkin dan Adam ta MDD da a kara yin shawarwari da hadin gwiwa da juna
2019-03-08 10:04:16 cri
A jiya Alhamis, zaunannen wakilin Sin dake ofishin MDD na birnin Geneva da sauran hukumomin kasa da kasa Yu Jianhua ya bayar da hadaddiyar sanarwa a madadin kasashe masu tasowa kimanin 50 a gun taron majalisar kare hakkin dan Adam ta MDD karo na 40.

Yu Jianhua ya yi nuni da cewa, ra'ayin bangare daya, da ra'ayin bada kariya, da ra'ayin nuna fushin fararen hula sun fara bazuwa a duniya a halin yanzu, don hakan an fi bukatar ra'ayin bangarori daban daban da hadin gwiwar dake tsakanin kasa da kasa don warware matsalolin da dan Adam suke fuskanta a tare. Kasashe masu tasowa suna son hada kan bangarori daban daban wajen kiyaye mabambantan ra'ayi da yin hadin gwiwa da shawarwari. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China