Kungiyar kawancen kasashen Larabawa, ta yi kira ga kasa da kasa su samar da kariya ga al'ummomin Falasdinu daga abun da ta kira da laifuka da take dokoki da Isra'ila ke yi.
Wata sanarwa da mataimakin Sakatare Janar na kungiyar ya fitar, ta ce akwai bukatar kasashen duniya da kwamitin sulhu na MDD su samar da kariya ga al'ummar Falasdinu wajen aiwatar da halaltattun kudure-kuduren kasa da kasa masu alaka da batun.
Abu Ali ya kuma soki abun da ya kira da bude wutan da Isra'ila ta yi a ranar Litinin, wanda ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa 2 da raunana wani guda a kauyen Kafr Ni'ma, dake wajen birnin Ramallah, dake yamma da kogin Jordan. (Fa'iza Mustapha)