in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin kasar Sin ya yi kira da a kara kokarin daidaita batun Syria ta hanyar siyasa
2019-03-02 16:35:02 cri
Wu Haitao, mataimakin wakilin kasar Sin a MDD, ya furta a jiya Jumma'a cewa, ya kamata MDD ta kara tattaunawa da kasar Syria, don gaggauta kafa majalisar tsarin mulki a kasar, da za ta wakilci bangarori daban daban, wadda kuma za ta karbu ga kowa.

Wu Haitao ya ce ta haka ne za a biya bukatun gwamnati da sauran bangarorin kasar, gami da kaddamar da wani shirin siyasa mai dorewa a kasar.

Jami'in, ya bayyana haka ne a wajen wani taron kwamitin sulhu na MDD mai alaka da aikin daidaita harkokin siyasa a kasar Syria, inda ya ce an kusa kawo karshen dukkan manyan rikice rikicen kasar. A cewarsa, kasar Sin ta ji dadin yadda kasashen Rasha da Turkiya da Iran suka sanar da ci gaba da yakar ta'addanci a Syria, da taimakawa aikin maida da tsarin siyasa kasar.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China