Kakakin fadar Saida Qarash ya bayyanawa kafofin watsa labaru a wannan rana cewa, a gun taron kolin AL da Turai da aka kammala ba da dadewa ba, wasu kasashen da abun ya shafa sun riga sun tattauna kan wannan batu. Wasu kasashen Larabawa da yawa na ganin cewa, kamata ya yi a warware rikicin Syria ta hanyar siyasa, da kuma sake farfado da zaman karko a kasar. (Bilkisu)