in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Amurka zai gana da takwarransa na Koriya ta Arewa a karo na biyu
2019-02-27 10:51:57 cri

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya isa birnin Hanoi, babban birnin kasar Vietnam jiya da dare, inda zai yi ganawa ta biyu tsakaninsa da shugaban Koriya ta Arewa tun daga yau Laraba zuwa gobe Alhamis.

Kafin hakan, fadar shugaban kasar Amurka wato White House ta sanar da cewa, shugaba Trump da shugaban kasar Koriya ta Arewa Kim Jong-un za su yi gajeren tattaunawa yau da dare, daga baya su ci abinci tare, sannan kuma su yi shawarwari a gobe 28 ga wata. A yinin yau kuma, shugaba Trump zai tattauna da shugabannin kasar Vietnam.

Kafin shugaba Trump ya tashi zuwa birnin Hanoi, ya bayyana cewa yana fatan za a cimma sakamako kan wannan shawarwari.

A watan Yunin shekarar 2018, Trump da Kim Jong-un sun yi ganawa ta farko a kasar Singapore tare da daddale hadaddiyar sanarwa, inda suka cimma daidaito kan kafa sabuwar dangantaka tsakanin Amurka da Koriya ta Arewa da kuma tsarin kiyaye zaman lafiya mai dorewa a zirin Koriya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China