in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika ta kudu ta bukaci kasashen Afrika su kyautata fannin yawon bude ido don janyo hankalin kasa da kasa
2019-02-26 10:21:21 cri

Hukumar kula da yawon bude ido ta Afrika ta kudu a jiya Litinin ta bukaci kasashen Afrika dasu yi iyakar kokarinsu wajen janyo hankalin masu sha'awar bangaren yawon bude ido na kasa da kasa.

Babbar jami'ar hukumar yawon bude ido ta Afrika ta kudu Amanda Kotze-Nhlapo, ta bayyana hakan a jiya Litinin yayin wani taron Afrika na shekarar 2019 wanda ya shafi batun bunakasa fannin yawon bude ido na Afrika wanda aka gudanar a lekgotla na birnin Johannesburg.

Ta ce, "Akwai masu sha'awar fannin yawon bude ido daga Afrika kana akwai su daga sauran sassan duniya. Don haka muka gayyaci dukkan masu sha'awar bunkasa wannan kasuwa da nufin ciyar da shiyyarmu da kuma nahiyarmu gaba."

Fiona Opati-Namiti, darakatar hukumar Villa Rosa ta kasar Kenya, ta fadawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, ya kamata kasashen Afrika su hada gwiwa don yin magana da murya daya ga duniya kuma su yi hadin gwiwa wajen karbar bakuncin muhimman tarurruka kuma dole ne su kawar da dukkan wasu kalubaloli dake kawo cikas ga fannin yawon bude ido kamar batun ka'idojin neman takardun izini na biza. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China