in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen labarawa da Turai zasu zurfafa hadin gwiwa don tunkarar kalubaloli
2019-02-26 09:40:58 cri

Shugabannin kasashen larabawa da na Turai sun sha alwashin zurfafa hadin gwiwa, don tunkarar kalubaloli da musayar kwarewa, a yayin da suka gudanar da taron kolin hadin gwiwa karo na farko na gamayyar kasashen larabawa da Turai wato (LAS)-EU, wanda ya gudana a ranakun Lahadi da Litinin a birnin Sharm el-Sheikh na kasar Masar.

A wata sanarwa da aka fitar bayan kammala taron, shugabannin kasashen Larabawan da na Turai sun bayyana kudurinsu na karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu a matakin koli da kuma sauran bangarorin hadin gwiwa a tsakaninsu.

Shugabannin sun sake jaddada aniyarsu na kyautata hadin gwiwar gamayyar kasa da kasa bisa ga tsarin kasa da kasa da kuma mutunta dokokin kasa da kasa domin dakile kalubalolin dake addabar duniya, wanda ya kunshi hadin gwiwa tsakanin LAS, EU, MDD da AU. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China