in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban DPRK ya tashi daga Pyongyang zuwa Hanoi don halartar taron sake ganawa tsakanin DPRK da Amurka
2019-02-24 20:18:34 cri
Da yammacin jiya Asabar shugaban kasar Koriya ta arewa (DPRK), Kim Jong Un, ya tashi zuwa Hanoi babban birnin kasar Vietnam, domin halartar zagaye na biyu na taron kolin tattaunawa tsakanin DPRK da Amurka, kamfanin dillancin labaran kasar Koriyar (KCNA) ne ya bada rahoton a yau Lahadi.

Kim, zai gana da shugaban kasar Amurka Donald Trump, a ranar 27 zuwa 28 ga watan Fabrairu. An gudanar da ganawar farko tsakanin shugabannin biyu ne a watan Yunin shekarar 2018 a kasar Singapore, inda ganawar ta haifar da kyakkyawan sakamako kan dangantaka a tsakanin kasashen biyu. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China