in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An jiyo karar ababen fashewa a arewa maso gabashin Nijeriya, yayin da aka fara kada kuri'a a kasar
2019-02-23 20:22:15 cri

An ji karar ababen fashewa da sanyin safiyar yau Asabar a birnin Maiduguri dake arewa maso gabashin Nijeriya, sa'o'i kafin fara kada kuri'a a zaben shugaban kasa da na 'yan majalisun tarayya a kasar dake yamacin Afrika.

An ji karar fashewar abubuwan ne da misalin karfe 6 na safe a Maiduguri, babban birnin jihar Borno. Inda ake fama da ayyukan kungiyar Boko Haram.

Al'ummar Nijeriya sun fara kada kuri'a ne da misalin karfe 8 na safiya, a kusan rumfunan zabe 120,000 dake fadin kasar. An dage zaben ne da mako guda a kan lokacin da tun farko aka shirya gudanar da zaben.

Shugaban kasar mai ci Muhammadu Buhari, wanda ke neman zarce a wa'adi na biyu, ya kada kuri'arsa a mahaifarsa ta Daura, dake yankin arewacin kasar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China