in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijeriya ta lashi takobin hukunta yaran da suka nemi kada kuri'a
2019-02-23 16:25:38 cri

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Nijeriya, ta ce za a tsare tare da gurfanar da duk wanda aka kama yana kada kuri'a kuma shekarunsa ba su kai ba, a babban zaben kasar.

Yayin wani taron manema labarai jiya a Abuja babban birnin kasar, Shugban hukumar INEC Mahmood Yakubu ya bukaci a bada rahoton irin wadannan yara nan take, a duk inda aka gansu a fadin kasar.

Mahmood Yakubu, ya ce hukumar na aiki da 'yan sanda domin kama yaran da shekarunsu bai kai ba da masu daukar nauyinsu, yana mai cewa za a tsare duk wani yaro ya yi korin a tantance shi ko kuma kada kuri'a.

Ya kara da cewa 'yan Nijeriya da shekarunsu suka kai 18 ne kadai za su iya kada kuri'a a zabe.

Shugaban ya kuma shawarci al'ummar kasar da su sa ido kan duk wadanda suka yi kokarin tada rikici, yana mai bukatar a dauke su hoto ko bidiyo a aike shafin website na hukumar INEC.

Samun yara masu kada kuri'a abu ne da aka saba gani a arewacin kasar, kuma ya zama ruwan dare ne saboda akwai wasu dake daukar nauyinsu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China