in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Cutar Ebola na ci gaba da yaduwa a Jamhuriyar Demokradiyyar Congo
2019-02-22 10:19:48 cri
Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta ce cutar Ebola na ci gaba da yaduwa a jamhuriyar Demokradiyyar Congo cikin matsakaicin yanayi, kuma ta na kara barazanar bazuwa a yankunan da ta barke.

Har yanzu, Katwa da Butembo dake arewa maso gabashin kasar, su ne yankunan da aka fi damuwa da su, yayin da ake samun karuwar a wuraren da babu yawan jama'a.

A cikin makonni 3 da suka gabata, an samu mutane 79 da suka kamu da cutar daga yankuna 40 dake cikin shiyoyin 12, sai dai babu sabon rahoton wani da ya kamu da cutar a Beni, daya daga cikin inda cutar ta fara barkewa. WHO na ganin wannan a matsayin ci gaba, la'akari da karfin barkewar cutar a yankin. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China